Isa ga babban shafi
Nigeria

An rufe makarantu 85 a jihar Borno saboda Boko Haram

Rahotannin da ke fitowa daga Borno a arewacin Nigeria na nuna cewa hukumomin Jihar sun rufe makarantun sakandare 85, har sai illa masha Allahu.Hukumomin sun dauki wannan matakin ne saboda fargabar hare hare, daga kungiyar nan ta Boko Haram. Rufe makarantun 85 zai sa yara fiye da dubu 120 su ci gaba da zama a gida, a jihar da ke fama da tashe tashen hankula, tsawon shekaru 5.Ko a shekarar bara, sai da gwamnan jihar ta Borno, Kashim Shettima yace ‘yan bindigan sun kona fiye da azuzuwa 800, wasu har fiye da sau 2. 

Gwamnan Jahar borno Kashim shetimma a lokacin da ya ke ta'adin da 'yan bindiga suka yi a jihar
Gwamnan Jahar borno Kashim shetimma a lokacin da ya ke ta'adin da 'yan bindiga suka yi a jihar REUTERS
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.