Bama neman agajin kowa kan gasar kwallon kafa a 2022 - Qatar
Qatar ta musanta rahotannin cewa tana tattaunawa da wasu kasashe makwabtanta dangane da yiwuwar hada gwiwa domin karbar bakuncin gasar cin kofin duniya ta shekarar 2022.
Wallafawa ranar:
Shugaban kwamitin dake lura da shirin Qatar na daukar nauyin gasar Nasser al-Khater, ya ce duk da cewa shugaban FIFA Gianni Infantino na fatan soma aiwatar da sauyin kara yawan kasashen da za su halarci gasar ta 2022 daga 32 zuwa 48, babu gaskiya cikin rahoton suna neman tallafin wasu kasashe.
Sai dai Infantino ya ce muddin karin yawan kasashen ya tabbata, hakan na nufin cewa za’a fafata wasanni 80 a gasar, sabanin 64 da hudu da ake yi a baya, dan haka dole makwabtan Qatar su karbi bakuncin wasu wasannin.
Gwamnatin Qatar ta ce tana kashe akalla dala miliyan 500 a kowane mako guda, kan gine-ginen da za’a yi amfani da su yayin karbar bakuncin gasar cin kofin duniyar a 2022.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu