Isa ga babban shafi

Sama da bakin haure 40 sun bace bayan kifewar kwale-kwalensu a ruwan Italiya

Majalisar Dinkin Duniya tace, sama da mutane 40 ne suka bace bayan da wani kwale-kwalen bakin haure ya kife a tsibirin Lampedusa na kasar Italiya.

Wasu 'yan ci rani da ke son tsallaka tekun Meditaraniya don shiga nahiyar Turai.
Wasu 'yan ci rani da ke son tsallaka tekun Meditaraniya don shiga nahiyar Turai. REUTERS - AYMAN AL-SAHILI
Talla

Wakilin Hukumar kula da ‘yan gudun hijara ta Majalisar Dinkin Duniya, UNHCR a Italiya Chiara Cardoletti tace tun ranar Alhamis ne kwale-kwalen ya kife kuma tace wani jariri aka haifa na cikin wadanda suka bata, Jirgin ruwan ya taso ne daga Sfax na kasar Tunisiya kuma yana dauke da bakin haure 46 daga kasashen Kamaru da Burkina Faso da Ivory Coast.

Flavio Di Giacomo, kakakin hukumar kula da shige da fice ta Majalisar Dinkin Duniya IOM, yace Kwale-kwalen ya kife ne saboda iska mai karfi da igiyar ruwa, inda aka kai wasu da suka tsira zuwa Lampedusa, wasu kuma an dawo da dasu Tunisia.

Tsibirin Lampedusa na kudancin Italiya na da tazarar kilomita 145 daga gabar tekun Tunisiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.