Isa ga babban shafi
Birtaniya

Birtaniya na cikin kasashen da ke yaki da ISIL

Birtaniya ta shiga sahun kasashen Amurka da Canada da ke yi wa Mayakan IS ruwan wuta da jiragen sama a Syria kamar yadda wata majiyar tsaro ta tabbatar, duk da majalisar kasar ta ki amincewa da matakin a shekarar 2013.

Jiragen yakin Amurka da ke luguden wuta akan mayakan IS a Syria
Jiragen yakin Amurka da ke luguden wuta akan mayakan IS a Syria US Army
Talla

Kakakin Firaministan kasar David Cameron ya ce jiragen kasar marar sa matuka na cikin jerin jiragen Amurka da ke yi wa mayakan IS luguden wuta.

Amma ma’aikatar tsaron kasar ta musanta zargin, tana mai cewa babu wani matuki jirgin Birtaniya a Syria.

Yanzu haka kuma wasu ‘Yan Majalisar kasar sun bukaci Ministan tsaron Birtaniya ya yi mu su bayani akan matakin bayan sun yi watsi da bukatar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.