Isa ga babban shafi
Nijar

Nijar za ta kafa gwamnatin hadin kai

Shugaban jamhuriyar Nijar Issoufou Mahamadou ya ce a shirye ya ke domin kafa gwamnatin hadin-kan kasa bayan nasarar da ya yi a zaben da aka gudanar a ranar Lahadin da ta gabata.

Shugaban kasar Niger Mahamadou Issoufou.
Shugaban kasar Niger Mahamadou Issoufou. AFP PHOTO / FAROUK BATICHE
Talla

Issoufou Mahamadou ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP cewa, yana fatan kafa gwamnatin da za ta kunshi ‘yan adawa domin tunkarar kalubalen da kasar ke fuskanta, da suka hada da tsaro da kuma tattalin arziki.

To sai dai Salah Amadou na gungun ‘ya adawa, ya ce ba wani zabe da aka gudanar ballantana su amince da Issoufou a matsayin shugaba.

Ga abinda ya ke cewa

01:04

Muryar Salah Amadou na 'yan adawar Nijar

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.