Isa ga babban shafi

Jakadan Najeriya a Morocco ya rasu

Jakadan Najeriya a Morocco, Alhaji Mansur Nuhu Bamalli ya rasu yana da shekaru 42 a duniya, bayan wata ‘yar gajeruwar rashin lafiya da ya yi.

Alhaji Mansur Nuhu Bamalli
Alhaji Mansur Nuhu Bamalli © The Cable
Talla

Kafin rasuwar Alhaji Bamalli, shi ne Magajin Garin masarautar Zazzau na yanzu, kuma kane ga sarkin Zazzau da ke jihar Kaduna a Najeriya  Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli.

Wata sanarwa daga fadar Mai Martaba Sarkin Zazzau  ta ce Mansur Nuhu Bamalli ya mutu ne a wani asibiti mai zaman kansa da ke birnin Lagos, a yayin da ya ke kan hanyarsa ta zuwa kasar Morocco.

Sanarwar ta kara da cewa za a sanar da lokacin jana’izarsa a nan gaba kadan.

Bamalli, wanda  tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ne ya nada shi a watan Oktoban shekarar da ta gabata ya rasu ya bar mata guda da ‘yaya biyu

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.