Isa ga babban shafi

Shugaba Tinubu ya janye daukacin jakadun Najeriya dake kasashen duniya

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya janye daukacin jakadun kasar dake kasashe daban-daban.Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Amb. Yusuf Tuggar, ya bayyana matakin ta bakin mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Alkasim Abdulkadir, a wannan Asabar.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu. 8/05/23
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu. 8/05/23 AP - Ben Curtis
Talla

A watan Yulin shekarar 2020 ne tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada jakadu 83 wadanda suka kunshi ma’aikatan diflomasiya 41 da jakadun siyasa 42 zuwa kasashe daban-daban.

An tura jami’an diflomasiyyar ne bayan Majalisar Dattawa ta tabbatar da su kamar yadda sashi na 171(2) (1c) da karamin sashe na 4 na kundin tsarin mulkin 1999 ya tanada.

Sanarwar da ta tabbatar da kiranye ga ilahirin jakadun ta ce: hakan na da nasaba da wasikar janye jakadan Najeriya a Burtaniya, Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, ya yi karin haske kan cewa duk jakadun su dawo gida bisa umarnin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

A cikin wasikar mai dauke da ranar 31 ga watan Agustan shekarar 2023, Ministan Harkokin Waje ya sanar da kawo karshen aikin Ishola a kasar Ingila kamar yadda shugaban kasar ya bukaci ya yi..

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.