Isa ga babban shafi
Najeriya

Ba zan sanya hannu a kasafin Najeriya ba- Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, ba zai sanya hannu  a kasafin kudin kasar na shekarar 2016 ba da majalisar dattawan kasar ta mika ma sa bayan ta amince da shi.

Shugaban Najeriya  Muhammadu Buhari tare da sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari tare da sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry. AFP PHOTO / STRINGER
Talla

Buhari ya fadi haka ne a birnin Washington na Amurka inda ya ce, zai duba kasafin filla-filla kafin ya sanya ma sa hannu.

A lokacin da ya ke ganawa da sakataren harkokin wajen Amurka Johan Kerry a jiya Alhamis, Buhari ya ce, ya na bukatar sake nazarin kasafin domin tabbatar da cewa ba a sauya bayanan da ke cikinsa ba.

Buhari ya kara da cewa, wasu jami’an gwamnati sun sauya wasu abubuwa da fadar shugaban kasa ta saka a cikin kasafin, inda suka sanya abinda suke bukata.

Shugaban ya jaddada cewa, zai duba kasafin da aka ware wa kowacce ma’aikata a Najeriya don tabbatar da cewa ya yi dai dai da abinda fadarsa ta gabatar wa majalisa tun a farko.

A bangare guda, shugaba Buhari ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da yaki da matsalar cin hanci da rashwa yayin da John Kerry ya ce, Amurka za ta taimaka wa Najeriya wajen mayar ma ta da kudaden da aka sace kuma aka boye su a bankunan Amurka.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.