Al’ummar Gombe na cikin fargabar harin boko Haram
al'ummar Gombe sun tashi cikin rudani da fargaba sakamakon karar harbe-harben Bindiga da suka ji daga sassa daban daban masu makwabtaka da su
Wallafawa ranar:
Rahotanni daga garin Gombe na cewar an shiga rudani a wayewar gari yau Assabar bayan da ‘ya’yan kungiyar Boko Haram suka kai hari a wani kauye mai suna Dadin kowa da ke daf da garin gombe.
An ce dai mutane sun gidime ana ta guje-guje, lura da cewar kauyen Dadin kowa na makwabtaka da Gombe ne.
Haka ma karar harbe-harben da aka ji daga bangaren Sojin Najeriya da ‘yan sanda, ya kara firgita jama’a, amma ya zuwa yanzu babu labarin ko wasu sun rasa rayukansu a cikin tashin hankalin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu