Isa ga babban shafi
Najeriya

Hukumar kare hakkin bil'adama a Najeriya ta gargadi Najeriya kan salwantar da Rayuka

Hukumar kare hakkin bil’adama ta tarayyar Najeriya ta fidda Rahoton cewar ya zuwa yanzu mutane 58 ne suka mutu a gangamin siyasa

newsbreak.ng
Talla

Wannan kuwa inji rahoton hukumar ya faru ne sakamakon tashe-tashen hankullan da ke da alaka da yadda ake gangamin yakin neman zaben shugaban kasa, gabanin a gudanar da zaben da ake kallo a matsayin zakaran gwajin dafi ga makomar Siyasar kasar.

A rahoton da hukumar ta fitar jiya Jumu’a ta bayyana cewar cikin kwanaki 50 na gangamin yakin neman zaben da aka gudamar, an samu tashin hankalin Siyasa akalla 61 a jihohi 22 na fadin kasar a yayin da mutane 58 suka rasa Rayukansu.

A lokacin da yake gabatar da Rahoton shugaban hukumar Chief Chidi Odinkalu, ya bayyana cewar nauyi ne day a rataya ga gwamnatin tarayyar Najeriya da ‘yan takara da jam’iyyun Siyasa da kuma jami’an tsaro su tabbatar da kare Rayuwar Tallakawan kasar da suka nuna tsananin kwadayin dorewar Dimokradiyya a cikin kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.