Isa ga babban shafi

Sama da Falasdinawa dari 7 hare-haren Isra'ila ya kashe a karshen mako

Daruruwan Falasdinawa sun rasa rayukansu a karshen mako, sakamako hare-haren sojojin Isra’ila a yankin Gaza, musamman kan birnin Khan Younis.

Wasu daga cikin Falasdinawa dari 7 da suka rasa rayukansu a hare-haren Isra'ila a yankin Gaza a karshen mako.
Wasu daga cikin Falasdinawa dari 7 da suka rasa rayukansu a hare-haren Isra'ila a yankin Gaza a karshen mako. AFP - MAHMUD HAMS
Talla

A baya dai kasashen Qatar da Masar sun samu nasarar shiga tsakani wajen kulla yarjejeniyar tsagaita wuta, wacce ta fara aiki a ranar 24 ga watan daya gabata.

Tsagaita wutar da ta bada damar musayar fursunini a tsakanin bangarorin Isra’ila da Hamas, sau biyu a na tsawaitata, sai dai a ranar Juma’ar da ta gabata ne ta kawo karshe.

Kafin  cimma yarjejeniyar tsagaita wutar, hare-haren Isra’ila ta sama da kuma kasa sun yi sanadiyar mutuwar Falasdinawa dubu 14, yawancinsu mata da kananan yara ne, sannan kimanin mutane miliyan daya da dubu dari 7 suka tsere daga gidajensu.

Daraktan yada labaran gwamnatin Gaza Ismail Al-Thawabta, ya shaidawa kafar Al Jazeera cewa sama da Falasdinawa dari 7 ne aka kashe a cikin sa’o I 24 da sake faro rikicin.

An dai bada rahoton ci gaba da ruwan bama-bamai da Isra'ila ke yi a yankunan Khan Younis da Rafah da kuma wasu bangarorin yankin Arewacin Gaza da ake zargin sojojin Isra’ila na kai wa hare-hare cikinsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.