Isa ga babban shafi
GASAR OLYMPICS

Za a takaita zirga zirgar ababan hawa a birnin Paris

FARANSA – Hukumomin dake shirya gasar Olympics da za'ayi a birnin Paris ta kasar Faransa a shekara mai zuwa, sun sanar da cewar za'a takaita zirga zirgar ababan hawa a sassan birnin da dama saboda yawan jama'ar da ake saran su halarci wasannin.

Hotan alamar Olympics da aka dauka a Paris a ranar 14 ga watan Satumbar shekarar 2017
Hotan alamar Olympics da aka dauka a Paris a ranar 14 ga watan Satumbar shekarar 2017 AFP - FRANCK FIFE
Talla

Shugaban 'yan sandan da zasu sanya ido wajen tabbatar da tsaro, Laurent Nunez yace masu dauke da tikiti ne kawai za'a bai wa damar shiga filayen wasanni, yayin da aka saka shingen da zai kare 'yan kallo da masu wasa.

Jami'in yace za'a hana zirga zirga a wurare da dama na birnin Paris da za'a gudanar da wadannan wasanni daban daban a yammaci da kuma tsakiyar birnin Paris.

Daga cikin yankunan da za'a hana zirga zirga gaba daya, akwai Place la Concorde dake tsakiyar Paris, inda za'a gudanar da wasan kwallon kwando da kuma rawar 'break dancing', sai kuma Trocadero da tsaunin Eiffel Tower da Champ-de-Mars.

Sai dai sanarwar tace za'a a bar masu amfani da kekuna su shiga inda suke so.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.