Isa ga babban shafi

Isra'ila ta kammala yi wa Gaza kawanya bayan kashe Falasdinawa 700

Rundunar Sojin Isra'ila ta sanar da kammala yiwa yankin Gaza kawanya bayan ruwan makaman roka da hare-hare ta sama da ta yiwa yankin daga daren jiya zuwa wayewar safiyar yau, inda ta kwace iko da shingen da Falasdinawa suka karya a ranar Asabar wanda ya raba yankin da cikin Isra'ila.

Akalla mutane 200 Isra'ila ta kashe cikin daren jiya zuwa yau kadai.
Akalla mutane 200 Isra'ila ta kashe cikin daren jiya zuwa yau kadai. AP - Ramez Mahmoud
Talla

Sanarwar ta rundunar Sojin Isra'ila na zuwa ne a dai dai lokacin da Hamas ke barazanar fara kashe fursunonin da mayakanta suka kamo daga cikin Isra'ila ciki har da mutanen kasashen ketare.

A bangare guda ma'aikatar lafiyar yankin na Gza ta sanar da kisan mutanen da yawansu ya haura 700 a hare-haren na Isra'ila ciki har da wasu 200 a daren jiya kadai.

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa yara dubu 1 da 300 na sahun mutum dubu 3 da 700 da hare-haren na Isra'ila suka jikkata baya ga wasu tarin kananan yara da mata da kuma dattijai wadanda hare-haren na Sojin Isra'ila ya kashe.

Tarin kananan yara na cikin wadanda hare-haren Isra'ila ya kashe a yankin na Gaza.
Tarin kananan yara na cikin wadanda hare-haren Isra'ila ya kashe a yankin na Gaza. REUTERS - IBRAHEEM ABU MUSTAFA

Yanzu dai Isra'ila ta sanar da daukar sabbin sojoji dubu 300 wadanda ta sanya a cikin dakarunta don kaluabalantar hare-haren na Hamas.

 

Kungiyar kasashen larabawa ta Arab League ta sanar da shirin gudanar da wani taron gaggawa kan halin da ake ciki a yankin na Gaza.

Masana dai na gargadin yiwuwar yakin ya iya zama mafi tsayi tsakanin bangarorin biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.