Isa ga babban shafi

Majalisar Dinkin Duniya ta amince da kawo karshen rundunar MUNISMA a Mali

Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya kada kuri’ar amincewa da kawo karshen ayyukan rundunar sojin Majalisar a Mali wato Minusma, kamar dai yadda gwamnati Mali ta bukata. 

Dakarun MUNISMA a yayin wani fareti da suka gudanar.
Dakarun MUNISMA a yayin wani fareti da suka gudanar. AFP - SIA KAMBOU
Talla

Kwamitin Tsaron ya kada kur’ar ne da gagarumin rinjaje domin kawo karshen ayyukan wannan runduna da aka kafa tun a shekara ta 2013, domin taimaka wa Mali ta yaki ayyukan ta’addanci da kuma wanzar da zaman lafiya a kasar. 

An dai kada Kuri’ar ne makonni biyu bayan da ministan harkokin wajen kasar Abdoulaye Diop, ya gabatar da bukatar hakan a gaban Majalisar, inda ya zargin rundunar ta Minusma da nuna gazawa a cikin ayyukanta. 

Karkashin wannan kuduri da aka amince da shi a yau jama’a, daga yau 30 ga watan Yuni rundunar ta kawo karshen ayyukanta, to sai dai ba kamar yadda Mali ta bukata na ganin an kammala aikin janye dakarun a cikin watanni uku ba, dakaru za su ci gaba da janyewa sannu a hankali har zuwa ranar 31 ga watan Disambar wannan shekara. 

Lokacin da aka faramahawarardangane da wannan batu, kasashenFaransa da Amurkasunbukaci a bai wadakarunwatanni 18 domin janyewa, indadagakarshe aka amince da watanni 6 watoranar 31 ga watan Disambamaizuwa. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.