Mali ta bukaci a gaggauta janye dakarun Majalisar Dinkin Duniya daga kasar
Kasar Mali ta bukaci gaggauta janye mata dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya daga kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Ministan harkokin wajen Mali Abdoulaye Diop ya yi wannan kira ranar Jumma'a ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, yana mai Allah wadai da " gazawar rundar wajen kawo karshen matsalolin tsaro dake addabar kasar na tsawon lokaci da ta dauka tana aiki a kasar.
Shugabannin soji dake mulkin Mali sun jima suna katange ayyukan dakarun MINUSMA a kasar tare da janye alaka da Faransa da ta yi wa kasar mulkin mallaka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu