Isa ga babban shafi
Brazil

An tsige Shugaban Majalisar wakilan Brazil

Kotun Kolin Brazil ta dakatar da shugaban Majalisar wakilan kasar Eduardo Cunha, wanda shine na gaba gaba wajen ganin an tsige shugabar kasar Uwargida Dilma Rousseff da ake zargi da karkata makudan kudade.

Dilma Roussef Shugabar kasar Brazil
Dilma Roussef Shugabar kasar Brazil Reuters/Ricardo Moraes
Talla

Kotu ta same shi da laifin kokarin hana gudanar da bincike akan sa saboda zargin da ake masa na cin hanci da rashawa.
Duk da yake dakatar da shi daga aiki ba zai iya hana yunkurin tsige shugabar ba, amma matakin ya dada fito da yadda matsalar cin hanci da rashawa tayi katutu a yan siyasar kasar Brazil.
Shugabar kasar Uwargida Dilma Rousseff na kokarin gani ta rike kujerar shugabancin kasar inda rahotanni suka tabbatar da cewa ta na kokarin gani ta shawo kan da dama daga cikin yan siyasa don gani an yi watsi da batun tsige ta.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.