An Sake Bude Filin Jiragen Sama na Brussels
An sake bude Filin sauka da tashin jiragen sama na Brussels dake kasar Belgium a yau lahadi bayan an rufe shi tun ranar 22 ga watan jiya a lokacin da aka kai kazamin harin kunar bakin wake da yayi sanadiyyar mutuwar mutane 32.
Wallafawa ranar:
Mutane biyu ne dai aka gano suka kai harin kunar bakin waken wanda kungiyar IS ta masu jihadi ta ce ita ta kitsa.
Tun a jiya shugaban filin jiragen saman Arnaud Feist ya sanar cewa yau lahadi ne za’a dan fara amfani da filin, inda jiragen saman uku za su tashi.
An dai dauki tsauraran matakan tsaro, kuma an umarci fasinjoji dasu kasance suna filin jiragen saman sao'i uku kafin jirginsu ya tashi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu