Isa ga babban shafi

Magatakardan MDD yana Burundi don nemo mafita a game da rikicin Congo

Magatakardan Majalisar Dinkin Duniya,  Antonio Guterres  ya sauka a kasar Burundi, inda ya tattauna da shugaban kasar a game da rikicin da ake a makwafciyarta, Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.

Magatakardan Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres,  da shugaban Burundi,  Evariste Ndayishimiye, a Bujumbura,ranar  6 ga Mayu,  2023.
Magatakardan Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, da shugaban Burundi, Evariste Ndayishimiye, a Bujumbura,ranar 6 ga Mayu, 2023. AFP - TCHANDROU NITANGA
Talla

A yayin ziyarsa ta farko a kasar, Guterres ya yi kira ga kungiyoyin da ke dauke da makamai a kasar da su ajiye makaman, kana ya ce dole ne a zage dantsi wajen kawo karshen rikicin da ake yi kasar.

Gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo na da dimbim arzikin karkashin kasa, wanda ake matukar nema a sassan duniya, lamarin da ake ganin ya kwadaita wa wasu kungiyoyi daukar makamai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.