Isa ga babban shafi

Faustin-Archange Touadéra na shirin yiwa kudin tsarin mulki gyaran fuska

A jamhuriyar Afirka ta Tsakiya yanzu haka ana cece-kuce biyo bayan bukatar Shugaban kasar na yiwa kudin tsarin mulkin kasar  gyara,Faustin Arkange Touadéra ya gabatarwa 'yan Majalisar dokokin kasar da shirin na sa watan da ya gabata.

Shugaban Jamhuriyar Tsakiyar Afirka  Faustin-Archange Toudéra.
Shugaban Jamhuriyar Tsakiyar Afirka Faustin-Archange Toudéra. Ludovic MARIN / AFP
Talla

‘Yan adawa da kungiyoyin farar hula sun yi watsi da shirin da suka ce majalisar wakilai basu da hurumi sai dai ta hanyar kuri’ar raba gardama. Inda ma tuni suka bukaci yayi murabus.

Wasu daga cikin jam’iyyoyin siyasa a kasar sun kalubalanci wannan tsarin da Shugaban kasar ke shirin aiwartar da shi ,sun bayyana cewa yin haka tamkar yiwa dimokuradiyya tarkade ne.

Kasar tsawon shekaru ta fuskanci rigigimu na siyasa da suka janyo juyin mulki  tareda hadasa yaki tsakanin kabilu wannan kasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.