Isa ga babban shafi
Afrika

Kotun Bangui ta yi watsi da takarar Francois Bozize

Kotun Jamhuriyar Afirka ta tsakiya ta yi watsi da bukatar takarar tsohon shugaban kasa Francois Bozize a zaben shugabancin kasar mai zuwa sakamakon tuhumarsa da aikata kisa da azabtar da mutane da kuma takunkumin da Majalisar Dinkin Duniya ta kakkaba masa.

François Bozizé, tsohon shugaban Afrika ta Tsakiya
François Bozizé, tsohon shugaban Afrika ta Tsakiya Simon Maina/AFP
Talla

Kotun fasalta kundin tsarin mulkin kasar ta gabatar da wannan hukumci ne, bayan da alkalan kotun suka sanar da soke takarar wasu karin yan takara 3 a zaben da zai gudana ranar 27 ga watan nan.

A watan Satumba na shekarar 2020 ne tsofin shugabanin kasashen Afrika ta tsakiya, Francois Bozize da Michel Djotodiya suka samu ganawa a babban birnin kasar Bangui.

Tsohon Shugaban kasar Michel Djotodiya musulmi na farko da ya shugabanci kasar ya dawo gida bayan da ya share kusan shekaru shida ya na gudun hijira a Jamhuriyar Benin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.