Isa ga babban shafi
Libya

MDD ta yi tayin shiga tsakani don sansanta rikicin siyasar Libya

Babbar jami'ar Majalisar Dinkin Duniya a Libya mai fama da rikici ta yi tayin shiga tsakani don sansanta rikicin siyasar da ya kunno kai tsakanin bangarorin biyu a kasar, bayan da aka samu kafuwar gwamnatoci guda 2 da suka fara gudanar da mulki a baya bayan nan.

Mataimakiyar Musamman ga Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya kan Harkokin Siyasa a Libya Stephanie Williams yayin halartar taron tattaunawa kan siyasar kasar a birnin Tunis, na kasar Tunisia Nuwamba 9, 2020.
Mataimakiyar Musamman ga Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya kan Harkokin Siyasa a Libya Stephanie Williams yayin halartar taron tattaunawa kan siyasar kasar a birnin Tunis, na kasar Tunisia Nuwamba 9, 2020. REUTERS - ZOUBEIR SOUISSI
Talla

Kiran na Stephanie Williams ya zo ne kwana guda bayan da majalisar dokokin Libya da ke gabashin kasar ta rantsar da sabon firaminista da nufin maye gurbin mai ci Abdulhamid Dbeibah, matakin da masu lura da al'amura ke fargabar zai iya jefa Libya cikin wani sabon rikici.

Cikin wasu jerin sakwanni da ta wallafa a shafinta na Twitter, Williams wadda take mashawarciya ta musamman ga sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres kan kasar Libya, ta yi gargadin cewa kafa gwamnatoci biyu masu adawa da juna ba shi ne matakin da zai warware matsalar kasar ba.

Jami’ar ta bukaci Majalisar Wakilai da ke gabashin kasar da kuma Majalisar zartaswa mai hedikwata a birnin Tripoli, da su zabi wakilai shida kowannen su, don kafa  kwamitin hadin gwiwa domin samar da matsaya kan sansanta rikicin siyasar da ka iya kazancewa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.