Isa ga babban shafi
Ivory Coast - Siyasa

Ivory Coast: An saki gwamman mutanen da aka kama kan rikicin zaben 2020

Shugaban Ivory Coast Alassane Ouattara ya sanar da sakin mutane da dama da aka kama yayin rikicin da ya biyo bayan zaben shugaban kasar da aka yi a shekarar bara.

Shugaban kasar Ivory Coast Alassane Ouattara tare da abokin hamayyarsa tsohon shugaba Laurent Gbagbo, a birnin Abidjan, 27/7/2021.
Shugaban kasar Ivory Coast Alassane Ouattara tare da abokin hamayyarsa tsohon shugaba Laurent Gbagbo, a birnin Abidjan, 27/7/2021. AFP - ISSOUF SANOGO
Talla

Kimanin mutane 100 suka mutu a rikicin siyasar mai nasaba da zaben da ya gudana a watan Oktoban da ya gabata, wanda shugaba Ouattara ya lashe a wa’adi na 3.

'Yan takara daga bangaren ‘yan adawa sun kauracewa zaben a waccan lokaci, bisa hujjar takaita wa’adin shugabancin kasar zuwa guda 2 da kundin tsarin mulkin kasar ta Ivory Coast yayi.

Jagororin ‘yan adawa da suka hada da Laurent Gbagbo da Henri Konan Bedie dukkansu tsaffin shugabannin kasar ne dai suka sakin fursunonin siyasar.

Gbagbo ya nemi sakin karin mutane fiye da 100, ciki har da wasu da ke da hannu a wani tashin hankalin zaben shekarun 2010 zuwa 2011.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.