‘Yan sandan Ivory Coast sun ceto yara 68 daga aikin bauta a gonakin Cocoa
‘Yan Sandan Ivory Coast sun ceto kanan yara akalla 68 da ake bautar da su a wasu manyan gonakin noman Cocoa a garin Soubre dake yammacin birnin Abidjan.
Wallafawa ranar:
Soubre na daga cikin yankuna masu arzikin Cocoa a Ivory Coast, inda a yanzu haka, gwamnati ke fafutukar yaki da bautar da yara kanana ko kuma tilasta musu aiki a gonakin noman albarkar gonar na Cocoa.
Bincike dai ya nuna cewar mafi akasarin kananan yaran da ake bautar da su wajen noman Cocoan a kasar ta Ivory baki ne daga makwafciyar ta Burkina Faso, wadanda ya kama ta a ce yanzu haka suna halartar makarantu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu