Dakarun Rwanda na Samun nasarar yaki da masu Jihadi a Mozambique
Dakarun Rwanda dake taimakawa kasar Mozambique yakar masu ikirarin jihadi sun ce kasa da wata daya suna samun nasara wajen fatattakan masu jihadin wadanda suke neman kassara Mozambique.
Wallafawa ranar:
A makon jiya sojan Rwanda suka taimaka aka sami nasarar kwato garin Awasse, wani karamin gari wanda masu jihadi suka kwace a bara.
Kakakin Dakarun Rwanda Kanar Ronald Rwivanga ya shaidawa kamfanin Dillancin labaran Faransa AFP cewa suna samun nasarar dannawa da kwace dukkan wurare dake yankin Cabo Delgado daga hannun masu ikirarin jihadi.
Ya fadi cewa sun sami nasara a wurare biyu kuma suna dab da mamaye Mocinboa da Praia, yankunan da suka dade hannun masu jihadi tun 12 ga watan Agusta na 2020.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu