Sabon jakadan Faransa ya kama aiki a Rwanda
Tun daga lokacin da shugaba Emmanuel Macron ya kai ziyara Rwanda daga ranar 27 ga watan mayun wannan shekara har ma ya gana da shugaban kasar Paul Kagame, ana iya cewa an samu kyautatuwar alaka tsakanin kasashen biyu, inda a jiya alhamis sabon jakadan Faransa ya fara aiki a birnin Kigali na kasar ta Rwanda.
Wallafawa ranar:
Bayan ganawarsa da shugaba Kagame, sabon jakadan Faransa a Rwanda Antoine Anfré ya shaida wa Christophe Karenzi na sashen Kiswaili na rfi cewa,bayan rahoton bincike na Duclert da kuma ziyarar da shugaba Macron ya kai, ana iya cewa an bude sabon babi na alaka tsakanin Faransa da Rwanda.
Har ila yau akwai hukumar AFD da ke gudanar da ayyukan raya kasa da za ta bude ofishinta a birnin Kigala kafin karshen wanan shekara.
Akwai kamfanoni da masana’antun Faransa da ke wannan kasa, kamar ‘’Bollore’’ Antoine Anfré y ace ya na da yakinin cewa za a samu sakamakon mai kyau.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu