Isa ga babban shafi
Libya

Libya ta bude babbar hanyar da ta hade gabashi da yammacin kasar

Gwamnatin Libiya ta bude babbar hanyar da ta sada yankunan gabashi da kuma yammacin kasar da suka jima a rabe, sakamakon yakin basasar da ya biyo bayan kifar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Mu’ammar Gaddafi a shekarar 2011.

Aikin bude hanyar da ta hade gabashi da yammacin Libya.
Aikin bude hanyar da ta hade gabashi da yammacin Libya. © MAHMUD TURKIA/AFP
Talla

Fira Ministan Libya Abdul Hamid Dbeibah ya jagoranci kawar da guma-guman duwatsu da kuma tarin kasar da aka yi amfani da su wajen raba yankunan na Yammaci da Gabashin Libya.

An dai shafe tsawon lokaci ana fafatawa tsakanin Sojojin Gwamnatin Libya da mayakan Janar Khalifa Haftar da ke iko da yankin gabashin kasar, kafin daga bisani a cimma yarjejeniyar sulhun da ta kai ga kafa sabuwar gwamnati a karkashin Fira Ministan Abdul Hamid.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.