Isa ga babban shafi
Faransa - Libya

Faransa zata taimakawa sabuwar gwamnatin Libya - Macron

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana aniyar sa ta taimakawa sabuwar gwamnatin Libya a tattaunawar da suka yi da sabon Firaministan da aka zaba Abdel Hamid Dbeidah da shugaban kasa Mohammed Younes el-Menfi.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron bayan tattaunawar kwamitin tsaron kasashen Faransa da Jamus ta hoton bidiyo
Shugaban Faransa Emmanuel Macron bayan tattaunawar kwamitin tsaron kasashen Faransa da Jamus ta hoton bidiyo Thibault Camus/Pool via REUTERS
Talla

Macron wanda ya taya shugabannin murnar nasarar da suka samu, ya jaddada matsayin Faransa na ganin an kawo karshen rikicin kasar da kuma fatar kasar tare da kasashen duniya ke da ita akan su.

Shugaban yace a shirye yake ya basu goyan baya wajen sauke nauyin dake kan su musamman sake hada kan kasar da hukumomin gwamnati wuri guda.

Kasashen Jamus da Italia da Faransa da Amurka da kuma Birtaniya sun bayyana cewar akwai aiki sosai a gaban sabbin shugabannin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.