Isa ga babban shafi

Shugaban Zimbabwe ya tsallake rijiya da baya

Shugaban Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya ce ya tsira daga yunkurin da akai na hallaka shi, a wani harin bam da aka kai kan taron jam’iyyarsa ta Zanu-PF a yau Asabar, inda aka jikkata mataimakinsa Kemo Mohadi da sauran shugabannin jami’yya.

Shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa.
Shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa. Jekesai NJIKIZANA/AFP
Talla

Mutane da dama ne suka jikkata bayan fashewar Bam din yayin taron yakin neman zaben da ya gudana a birnin Bulawayo na biyu mafi girma a kasar ta Zimbabwe inda ake gangamin zaben shugabancin kasar da aka shirya za a yi a karshen watan Yuli mai zuwa.

Har yanzu dai jami’an agaji ko bangaren gwamnati basu bayyana adadin wadanda suka jikkata a harin ba.

Zaben shugabancin Zimbabwe da za a yi a ranar 30 ga watan Yuli mai kamawa, shi ne na farko a kasar, tun bayan da tsohon shugaba mai murabus, wato Robert Mugabe ya dare shugabancin kasar a shekarar 1980.

Harin bam din dai ya zo ne sa’o’i kalilan, bayan da aka kai makamancinsa a birnin Addis Ababa, kan taron gangamin goyon bayan sabon Firaministan Habasha Abiy Ahmed, inda akalla mutane 83 suka jikkata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.