Isa ga babban shafi
Zimbabwe

An bayyana ranar gudanar da zabubuka a kasar Zimbabwe

Mujallar wallafa labarai da kudurorin gwamnati, ta ce shugaban kasar Emmerson Mnangagwa ne ya amince da ranar ta 30 ga watan yuli domin gudanar da zaben shugaban kasa, na ‘yan majalisa da kuma na kansiloli.

Shugaban Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa, lokacin da ya halarci taron Davos, 24 janunari 2018.
Shugaban Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa, lokacin da ya halarci taron Davos, 24 janunari 2018. REUTERS/Denis Balibouse
Talla

Wannan dai zai kasance karo na farko da za a gudanar da zabubuka a kasar ta Zimbabwe ta bayan kawar da Robert Mugabe daga madafun iko.

Tuni Kungiyar Tarayyar Turai ta bayyana aniyarta ta tallafa wa kasar domin samun nasarar gudanar da wadannan zabubuka, da suka hada da samar da kudade da kuma kwararri domin shirya zaben a cikin kyakkyawan tsari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.