Isa ga babban shafi
Najeriya-Afrika ta kudu

An kara kashe wani dan Najeriya a Afrika ta kudu

Al’ummar Najeriya mazauna Afrika ta kudu sun tabbatar da kone wani dan Najeriya Clement Nwaogu wanda aka bankawa wuta da ransa har ya mutu a hare-haren kin jinin baki da ‘yan Afrika ta kudun ke ci gaba da kai wa kan baki mazauna kasar.

Mr Clement Nwaogu, dan Najeriyar da wasu tsageru suka bankawa wuta a Afrika ta kudu.
Mr Clement Nwaogu, dan Najeriyar da wasu tsageru suka bankawa wuta a Afrika ta kudu. NAN
Talla

Da ya ke tabbatar da hakan ga kamfanin dillacin labaran Najeriyar NAN, Habib Miller sakataren yada labaran kungiyar ‘yan Najeriyar mazauna Afrika ta kudu, ya ce lamarin ya faru ne a yankin arewa maso yammacin Rustenburg inda maharan suka far masa da muggan makamai kafin daga bisani su banka masa wuta.

Wasu shaidun gani da Ido a cewar Mr Habib sun ce sai da Clement ya nemi daukin jami’an ‘yansandan kasar amma suka ki agaza mishi.

Tsawon lokaci kenan dai wasu tsageru a kasar ta Afrika ta kudu ke aiwatar da kisan gillar kan ‘yan Najeriya ba kuma tare da daukar wasu kwararan matakai daga gwamnatocin kasashen biyu don dakatar da su ba.

A cewar Mr Miller har yanzu akwai ‘yan Najeriyar 14 da jami’an ‘yansandan Afrika ta kudun ke rike da su sakamakon zanga-zangar adawa da kisan da ake musu da suka yi a watan Fabarairu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.