An garkame 'yan Najeriya 400 a Afrika ta Kudu
Mnistan cikin gidan Najeriya Janar Abdulrahman Danbazau mai ritaya, ya ce, kimanin ‘yan kasar 400 ne ke tsare a gidan yarin Afrika ta Kudu sakamakon aikata laifuka daban-daban.
Wallafawa ranar:
Danbazau ya sanar da haka ne bayan wata ziyara da tawagarsa ta kai Afrika ta Kudu don tattauana kan farmakin da ake kai wa baki a kasar da suka hada da ‘yan Najeriya.
A cewar Ministan, daga cikin wadanda aka garkame a gidan yarin, akwai wadanda ake zargi da karuwanci da kuma safarar miyagun kwayoyi.
Danbazau ya kara da cewa, fursunonin za su kammala wa’adinsu na zaman kaso a Afrika ta Kudu saboda babu da wani shirin musayar fursunonin tsakanin kasashen biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu