Isa ga babban shafi
Najeriya

An garkame 'yan Najeriya 400 a Afrika ta Kudu

Mnistan cikin gidan Najeriya Janar Abdulrahman Danbazau mai ritaya, ya ce, kimanin ‘yan kasar 400 ne ke tsare a gidan yarin Afrika ta Kudu sakamakon aikata laifuka daban-daban. 

'Yan Afrika ta Kudu na kai wa baki 'yan cirani farmaki da suka hada da 'yan Najeriya
'Yan Afrika ta Kudu na kai wa baki 'yan cirani farmaki da suka hada da 'yan Najeriya ibtimes.co.uk
Talla

Danbazau ya sanar da haka ne bayan wata ziyara da tawagarsa ta kai Afrika ta Kudu don tattauana kan farmakin da ake kai wa baki a kasar da suka hada da ‘yan Najeriya.

A cewar Ministan, daga cikin wadanda aka garkame a gidan yarin, akwai wadanda ake zargi da karuwanci da kuma safarar miyagun kwayoyi.

Danbazau ya kara da cewa, fursunonin za su kammala wa’adinsu na zaman kaso a Afrika ta Kudu saboda babu da wani shirin musayar fursunonin tsakanin kasashen biyu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.