Isa ga babban shafi
Lake Chad

Amurka ta sake tallafa wa yankin tafkin Chadi

Gwamnatin Amurka ta sake ware Dala miliyan 92 don tallafa wa wadanda ke fama da matsaloli saboda rikice-rikice da karancin abinci a Najeriya da kuma kasashen yankin tafkin Chadi.

Wasu daga cikin masu fama da matsaloli saboda rikicin Boko Haram a Najeriya
Wasu daga cikin masu fama da matsaloli saboda rikicin Boko Haram a Najeriya SIA KAMBOU / AFP
Talla

Wadanda za su ci gaciyar tallafin sun hada da masu fama da rikicin Boko Haram musamman ‘yan gudun hijira da ke samun mafaka a sansanoni daban-daban.

Za a yi amfani da kudaden wajen samar da abinci da ruwan sha da matsugunai da kuma magunguna ga mabukatan.

Sama da mutane miliyan 6 ne cikin bukatar abinci da gaggawa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi sakamakon halin da rikicin Boko Haram ya jefa su a ciki.

Majalisar Dinkin Duniya ta kiyasta cewa, ana bukatar tallafin Dala biliyan 1 nan da shekara mai zuwa don biyan bukatun wadannan mutanen da ke fama da matsalolin.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.