Isa ga babban shafi
Najeriya

Mutane milyan biyar ne ke bukatar tallafi a arewa maso gabashin Najeriya

MDD ta ce ana bukatar sama da dala milyan dubu daya a shekara mai zuwa domin taimakawa jama’ar da ke fama da matsaloli sakamakon rikicin Boko Haram a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Wasu kananan yara da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu
Wasu kananan yara da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu
Talla

Mataimakin shugaban ofishin kula da ayyukan jinkai na na MDD Peter Lundberg, ya bayyana a wata sanarwa cewa akalla mutane milyan 5 ne za su kasance a cikin hali na bukata cikin shekara mai kamawaa yankin tare da yin kira ga kasashen duniya da kuma masu zaman kansu domin taimakawa.

Sanarwar ta bayyana jihohin Borno, Yobe da Adamawa a matsayin wadanda ke cikin hali na bukatar samun taimako.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.