Boko Haram ta kashe sojojin Kamaru 6
Kungiyar Boko Haram ta kai wani kazamin hari kan sansanin sojin hadin-kai na kasashen tafkin Chadi da ke tsibirin Darak, inda ta kashe sojojin kasar Kamaru guda 6.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce, akwai daya daga cikin ‘yan kungiyoyin sa-kai da ke taimakawa jami’an tsaron da aka kashe a harin.
Wannan na zuwa a yayin jami’an tsaro a Kolofata suka harbe wani da ke kokarin kai harin kunar bakin wake kusa da inda soji ke binciken ababan hawa akan iyaka da Najeriya.
Sojojin Kamaru na cikin rundunar hadin guiwa ta kasashen Chadi da Nijar da Najeriya da kuma Benin da ke fada da mayakan Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu