Somalia
Mutane sun mutu a harin Bam a Somalia
An kai harin Bam a lokacin da mutane ke tsakiyar cin kasuwa a Mogadishu na kasar Somalia tare da kashe Mutane takwas.
Wallafawa ranar:
Talla
Mai Magana da yawun ‘yan sanda Yankin da aka kai harin Ibrahim Mohammed, ya ce akasarin wadanda suka mutu fararen hula ne, kuma akwai da dama da suka jikkata.
A cewar jami'an kiwon lafiya, Alkallumar mamatan zai iya kai wa 30.
Kawo yanzu dai babu wata kungiyar data dau alhakin harin, sai dai ana zargin mayakan al-shabaab wanda ke yawaita kaddamar da hare-hare a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu