Isa ga babban shafi
Somalia

An kai harin Bam yayin taro kan tsaro a Mogadishu

Kungiyar Al-shabab ta kai hari a wani otel da ke kusa da fadar shugaban kasar a birnin Mogadishu, Harin daya halaka mutane 22 a wannan talata. 

Wasu daga cikin sojin Somalia da na Tarayyar Afrika AU
Wasu daga cikin sojin Somalia da na Tarayyar Afrika AU Reuters/路透社
Talla

Wannan dai ba shi ne karo na farko ba, da ‘yan kungiyar ta Alshabab ke kai hari a wannan otel da ake sauke manyan baki da kuma sauran jami’an gwamanati a cikinsa ba.

Rahotanni sun ce ana gudanar da wani taro kan yadda za’a shawo kan matsalolin tsaron kasar, a dai dai lokacin da aka kai harin.

Kimanin shekaru biyar da suka gabata, dakarun Tarayyar Afrika AU suka samu nasarar korar mayakan al-Shabbab daga babban birnin Somalia Mogadishu, sai dai har yanzu mayakan suna cigaba da kai hare-haren kunar bakin wake, da kuma tada bama bamai a sassan kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.