Nijar
Rundunar hadaka ta fara aikin kakkabe Boko Haram
Rundunar sojin jamhuriyar Nijar ta baynanna cewa, rundunar hadakar kasashe ta fara aikin kakkabe kungiyar Boko Haram a kan iyakar kasar da Najeriya.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban tsare tsare na sojin da aka girke a yankin Diffa, Birgediya Janar Abdou Sidikou Issa ya sanar da haka a jiya Talata.
Janar Issa ya kara da cewa, sojojin Najeriya da Chadi na cikin rundunar domin yi wa mayakan na Boko Haram taron dangi.
Kungiyar Boko Haram na ci gaba da kaddamar da hare hare a wadannan kasashen, inda suka hallaka jama’a da dama tare da tilasta wa wasu kaurace wa gidajensu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu