Isa ga babban shafi
Kamaru

An an fadada dokar haramta amfani da hijabi a kasar Kamaru

Mahukuntan kasar Kamaru sun sake fadada dokar haramta amfani da hijabi ko burqa, a kokarin da suke yi na kawar da ‘yan kungiyar Boko Haram, dake ci gaba da kai hare haren kunar bakin wake a yankunan kasar.

Wata mace. sanye da Hijabi ko Burqa
Wata mace. sanye da Hijabi ko Burqa AFP/Peter PARKS
Talla

Wannan matakin na zuwa ne kasa da wata daya, bayan da wasu mata ‘yan kunar bakin wake, sanye da hijabin, suka tayar da bama bamai a wani yankin dake kan iyakar kasar da Nigeria, daga arewaci, inda suka hallaka mutane 11.
Gwamnan Lardin Gabas daya jagoranci taron kwamitin tsaron yankin, da ya sami halartar manyan malaman addin Isalama, ya bi sawun takwarorisa na Arerwaci da Yammacin kasar, na haramta sanya hijabin.
Mai magana da yawun gwamnatin lardin yammacin kasar, yankin da birnin Douala yake Mireille Bisseck, yace daga yanzu an hana dinkawa, da sanya hijabin a kasar.
Bisseck ya kuma ce za a kara sa ido kan kiran sallah da ake yi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.