Isa ga babban shafi

An nada Guy Scott a matsayin shugaban rikon kwaryan Zambia

Majalisar zantarwa ta kasar Zambia ta baiwa Guy Scott rikon kwayan shugabancin kasar, sakamakon mutuwar tsohon shugaban kasar, Michael Sata, wanda ya rasu a birnin London.Guy Scott, zai kasance farin fatan na farko daya mulki wata kasa a nahiyar Afrika, karkashin mulkin demokradiyya.An haifi Dr. Guy Lindsay Scott a ranar 1 ga watan Yunin shekara ta 1944, a garin Livingston dake kasar zambia. Mahaifinshi, Alec Scott yazo garin ne a shekara ta 1927 yayinda mahaifitarsa, Grace Scott itama tayi hijara zuwa garin a shekara ta 1940sabon shugaban kasar dai ya kammala karatunsa na farko a kudancin kasar Rhodesia a wancan lokacin, wanda daga bisani ta koma Zimbabwe.Har ila yau Guy Scott yayi karatu a jami’ar Cambridge dake Birtaniyya, inda ya karbi digiri a fannin tattalin arziki.Mahaifinsa ne ya karfafa masa gwiwa wajan shiga harkar siyasa a kasar ta Zambia, bayan ya kasance mutum na farko daya samar da jaridun dake sukan mulkin mallakan a kasar.A shekara ta 1965 ne Guy Scott ya shiga cikin gwamnatin kasar inda ya fara aiki a matsayin mai tsare-tsare a ma’aikatar kudi ta kasar.A shekara ta 1991 ya wakilci mazabar Mpika a majalisar dokoki, karkashin jam’iyar MDD.Daga baya Guy Scott ya bar jam’iyar ta MDD inda ya koma jam’iyar PF, data bashi damar samun mukamin mataimakin shugaban kasa a shekara ta 2011.A jiya, bayan mutuwar tsohon shugaban kasar, Michaael sata, ya zamo farkon farin fatan da zai mulki wata kasa a nahiyar Afrika a mulkin demokradiyya. 

Shugaban rikon kwaryan kasar Zambia, Guy Scott
Shugaban rikon kwaryan kasar Zambia, Guy Scott Wikimedia Commons
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.