Isa ga babban shafi
Zambia

Kotun Zambia ta wanke Rupiah Banda daga zargin karbar cin hanci da rashawa

Kotu a kasar Zambia a yau ta wanke tsohon shugaban kasar Rupiah Banda, game da zargin da ake yi ma sa na karbar wasu motoci domin gudanar da yakin neman zabe.

Tsohon shugaban kasar Zambia, Rupiah Banda a tsakiya
Tsohon shugaban kasar Zambia, Rupiah Banda a tsakiya Photo AFP / Joseph Mwenda
Talla

An zargi Banda da karbara motocin ne ba a kan ka’ida ba daga wani kamfanin gine-gine mallakin kasar China.

Banda dan kimanin shekaru 76 a duniya, ya mulki kasar Zambia daga shekarar 2008 zuwa 2011, kuma ana zargin cewa ya yi amfani da mukaminshi domin karbar motocin daga wannan kamfani kafin kotun ta wanke shi a yau.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.