Kasa ta binne mahaka ma’adinai 9 a Zamfara
Rahotanni Daga Jahar Zamfara a Shiyar arewa maso yammacin Najeriya, sun ce akalla mutane Tara kasa ta rufe a kauyen Ruwan Dorawa, karamar hukumar Mulki taMaru, yayin da suke kokarin hako zinare ba tare da izini ba.
Wallafawa ranar:
Wannan na zuwa ne kwana guda bayan wasu mutane biyu sun yi nasarar hako zinar da kudin sa ya kai Naira Miliyan Biyu da Dubu Dari Uku.
Bayanai sun ce, da Asubahi aka yi kururuwar kai dauki ga mahakan goma da kasa ta binne, amma ba’a iya ciro su ba sai da azahar, kuma kafin nan mutane 9 sun mutu, Mutum daya ne ya tsira da ransa, kuma yana waknce a gadon asibiti.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu