An kara samun arangama tsakanin mabiya Shi'a da jami'an tsaro a Najeriya
An kara samun arangama tsakanin mabiya Shi’a da jami’an ‘Yansanda a Abuja babban birnin Najeriya, bayan wata zanga-zanga da suka kara gudanarwa yau don neman sakin jagoransu Sheikh Ibrahim Yakubu Zakzaky.
Wallafawa ranar:
Wanann dai shi ne karo na biyu da mabiya Shi’an suka gudanar da zanga-zanga cikin kasa da kwana goma inda a ranar 16 ga watan Aprilu jami’an ‘yansanda suka kame akalla mabiyan 15 bayan zanga-zangar da ta kai ga barnata kadadrorin jama’a da na gwamnati.
Jami'an tsaron sun yi amfani da karfin tuwo don tarwatsa masu zanga-zangar kamar yadda ya faru a makon jiya inda aka yi amfani da hayaki mai sanya hawaye don tarwatsa su.
Hukumomin kare hakkin dan adam dai na ganin gwamnatin Najeriyar ta ki mutunta umarnin da aka bata na sakin Sheikh Ibrahim Zakzaky, ko da ya ke dai tana ikirarin cewa tana kare lafiyarsa ne la'akari da cewa rayuwarsa na cikin hadari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu