Barcelona za ta bude makarantar kwallo a Lagos
Tawagar Kungiyar kwallon kafar Barcelona ta kasar Spain sun isa birnin Lagos dake Najeriya da labarin bude makarantar horas da ‘yan wasan kwallon kafa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Gwamnan jahar Lagos Akinwumi Ambode ne ya karbi tawagar a ofishin sa dake Alausa, Gwamnan ya kuma bayyana farin cikinsa da wannan ci gabar inda ya kara jadadda goyon bayan gwamnatin Lagos ga al'ammuran wasanni.
Wannan dai shine karon farko da Barcelona ke bude kwallejin da zai mayar da hankali kan horas da ‘yan wasan kwallon kafa a Afrika.
Najeriya na daga cikin kasashen Afrika dake da shahararrun 'yan wasan Kwallo a Duniya, ana kuma da dinbin magoya bayan kungiyar wasan kwallon Barcelona a kasar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu