Isa ga babban shafi
EGYPT

An yanke hukuncin daurin shekaru uku akan ma'aikatan Aljazeera

A yau asabar ne wata kotu a kasar Masar ta yankewa  ma’aikatan tashar talabijin din Aljazeera 3 hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari, saboda samun su da laifin yada labaran karya acewar gwamnatin kasar.

Ma'aikatan Aljazeera a gidan yari
Ma'aikatan Aljazeera a gidan yari
Talla

Ma’aikatan sun hada da Mohammed Fahmy dan kasar Canada da Baher Mohammed dan kasar Masar, yayin da Peter Greste, dan Australia ya koma kasar sa.

Tuni dai Kasashen duniya suka nuna rashin amincewarsu tare da yin Allah wadai da hukuncin yayin da Giles Trendle, shugaban gudanarwar tashar ta Aljazeera ya bayyana hukuncin a matsayin bakar rana ga bangaren shari’ar Masar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.