Isa ga babban shafi
G5-SAHEL

Macron ya bukaci cika alkawarin da aka yi na tallafawa G5 Sahel

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bukaci kasashen duniya da suka yi alkawarin bada agajin kudi da kayan aiki ga rundunar G5 Sahel da ke yaki da ta’addanci a Mali da su gagaguta cika alkawarin su.

Kawo yanzu dai daga cikin kasashen da suka yi alkwarin tallafawa rundunar Saudi Arabia ce kadai ta cika ta hanyar bayar da yuro miliyan dari.
Kawo yanzu dai daga cikin kasashen da suka yi alkwarin tallafawa rundunar Saudi Arabia ce kadai ta cika ta hanyar bayar da yuro miliyan dari. REUTERS/Grigory Dukor
Talla

Shugaba Macron ya shaidawa manema labarai bayan ganawa da shugaban Nijar Mahamadou Issofou cewar babu abinda su ke bukata cikin gaggauwa da ya wuce kudaden da rundunar za ta yi aiki da su.

Macron ya ce kudin da kungiyar kasashen Turai ta bayar anyi amfani da su wajen fara aikin rundunar, amma yanzu haka suna bukatar karin kudade.

Shugaban Nijar Mahamadou Issofou ya ce suna bukatar gabatar da euro miliyan 420 da akayi alkawari wajen gidauniyar taimakawa rundunar.

Issofou ya ce ya zuwa yanzu kasar Saudi Arabia ce kawai ta cika alkawarin ta na bada euro miliyan 100 wanda za’ayi amfani da su wajen sayan kayan aiki ga dakarun.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.