Joshua ya ce lokaci ya yi da ya kamata su dambace da Tyson
Shahararren dan damben boksin na kasar Ingila, dan asalin Najeriya, Anthony Joshua ya kalubalanci takwaransa Tyson Fury, inda ya ce yanzu ne lokacin da ya dace su gwada kwanji ta wurin gwabza dambe.
Wallafawa ranar:
Tattaunawa tsakanin Oleksandr Usyk, da Fury a kan yiwuwar fafatawa ta wargaje a makon da ya gabata.
Joshua, mai shekaru 33, zai dambace ne da takwaransa na Amurka, Jermaine Franklin a ranar Asabar, wasansa na farko a cikin wannan shekarar Kenan.
Ya ce babu wani lokaci da ya fi dacewa su shiga filin daga da Fury face yanzu, domin debe takaicin wargajewar wancan tattaunawa.
A shekarar da ta gabata, Joshua ya tattauna da Fury a kan dambacewa, amma suka gaza cimma matsaya, saboda haka Fury ya dambace da Derek Chisora a filin wasa na Wembley a watan Disamba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu