Anthony Joshua ya amince da fita daga gasar zakarun boxing na Duniya
Anthony Joshua ya amince cewa ya fita daga gasar zakarun ‘yan damben boxing na duniya, domin mayar da hankali kan sake shirin tunkarar kalubalen da ke gabansa.
Wallafawa ranar:
Joshua ya yi fafatawa ta karshe a cikin watan Agusta, inda ya sha kashi a Hannun Oleksander Usyk, karo na biyu a jere abinda ya say a kasa kwato kambunsa na WBA, WBO, IBF da IBO.
Daga baya Tyson Fury ya yi wa Joshua tayin su kara akan kambun WBC, amma ‘yann kasar Birtaniyar suka kasa cimma matsaya kan yiwuwar fafatawar damben ta ajin masu nauyi.
A halin yanzu dai an alakanta Joshua, mai shekaru 33, da yiwuwar sake karawa da Dillian Whyte, wanda shi Joshuan ya taba shank aye yayin karawarsu a lokacin da ke bako a fagen Damben na Boxing, sai dai a shekarar 2015 ya dauki fansar doke shi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu