Fury ya nemi a biya shi fam miliyan 500 kafin sake komawa dambe
Fitaccen dan damben boxing a duniya dan asalin Birtaniya Tyson Fury, ya bayyana cewa sai an biya shi fam miliyan 500 muddin ana bukatar ya sake komawa fagen wasan dambe.
Wallafawa ranar:
Fury mai shekaru 33, na cigaba da nanata cewar zai yi ritaya daga wasan damben boxing bayan da ya samu nasarar doke Dillian Whyte a filin wasa na Wembley a cikin watan Afrilu.
Gwarzon gasar damben ajin masu nauyi ta WBC ya yi wa magoya bayansa bazata a lokacin da ya bayyana matakinsa na yin ritaya, sai dai daga bisani ya ce a shirye yake ya koma fili domin fafata wasa na musamman da Anthony Joshua, idan har za a biya shi fam miliyan 200.
A halin yanzu kuma Tyson Fury ya daga darajar kudin da ya nema zuwa fam miliyan 500.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu