Isa ga babban shafi

Zakarun Turai: Liverpool da Real Madrid za su yi karon batta a Paris

Yau za kece raini tsakanin Liverpool da Real Madrid a wasan karshe na gasar cin kofin zakarun Turai a birnin Paris.

Dan wasan Gaba na Real Madrid Karim Benzema da kuma Virgil Van Dijk, mai tsaron baya na kungiyar Liverpool.
Dan wasan Gaba na Real Madrid Karim Benzema da kuma Virgil Van Dijk, mai tsaron baya na kungiyar Liverpool. AFP - SERGEI SUPINSKY
Talla

Liverpool dai na neman lashe kofin na gasar Zakarun Turai ne karo na 7, a yayin da Real Madrid ke fatan ta lashe kofin na 14.

Ana sa ran ‘yan kallo kimanin dubu 80 ne za su hallara a filin wasa na ‘Stade de France’ a birnin Paris domin ganin yadda za ta kaya a wannan babban wasa.

Jami'an 'yan sanda akalla dubu 7,000 ne za su kasance a bakin aiki domin tabbatar da doka da oda yayin fafatawar tsakanin Liverpool da Real Madrid.

Wasan, wanda shi ne irinsa karo na biyu da za a yi tsakanin tawagar ta Jurgen Klopp da Carlo Ancelotti, da fari an tsara buga shi ne a filin wasa na Gazprom da ke St Petersburg a Rasha, amma aka mayar da shi filin wasa na ‘Stade de France’ bayan da Rasha ta mamaye Ukraine a watan Fabrairu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.