Aubameyang ya fice daga gasar AFCON a Kamaru
An sahale wa dan wasan gaba na Arsenal Pierre Emerick Aubameyang da ya fice daga tawagar Gabon da ke fafatawa a gasar cin kofin Afrika a Kamaru sakamakon fama da cutar Korona.
Wallafawa ranar:
Yanzu haka Aubameyang zai koma London domin ci gaba da samun kulawa karkashin kungiyarsa ta Arsenal kamar yadda kocin tawagar Gabon ya bayyana a yau Litinin.
Kazalika Gabon ta mayar da dan wasanta na tsakiya Mario Lemina zuwa kungiyarsa ta Nice da ke Faransa, bayan dan wasa ya gaza buga ko da minti guda a wasanni guda biyu da kasarsa ta yi da Comoros da Ghana a gasar ta cin kofin Afrika.
Shi ma dai Lemina na fama ne da cutar Korona, abin da ya hana shi haskawa a gasar ta Afrika.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu